Ta’aziyyar Sambo Wali Giɗaɗawa

    Gabatarwa

    Alhaji Muhammadu Sambo Wali Giɗaɗawa fitaccen malami ne, fitaccen marubuci, kuma masanin tarihin ƙasar Hausa da Daular Sakkwato. A cikin Ƙungiyar Marubuta da Manazarta Waƙoƙin Hausa su ne dattawan marubuta. Ya yi koyarwa a firamare da ɓangaren Cibiyar Nazarin Addinin Musulunci, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato. Ya yi wa Gidan Rediyon Rima Sakkwato gudummuwa gawurtacciya da ko’ina an ji ta. A fannin wasanni da faɗakarwa, Malam Sambo ya yi gudunmuwa sosai. A ɗan nawa bincike, cikin manazartan zamaninmu babu wanda ya kai Malam Sambo sanin tarihin ƙasar Hausa ta Gobir da Daular Sakkwato. Don haka nake ganin ko bayan rasuwarsa, ya kamata Jami’ar Sakkwato ta ba shi yabo da digirin Girmamawa (Dr.). Allah ya gafarta wa Malam Sambo Wali Giɗɗawa. Amin.

    author/Aliyu Muhammadu Bunza

    journal/Zauren Waƙa 4(2) | July 2025 |

    Pages